1 Chronicles 17:16 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Sarki Dawuda ya shiga ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Wane ne ni, ya Ubangiji Allah, kuma wane ne iyalina, da ka kawo ni har zuwa nan?
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ سَرْكِے دَاوُدَ يَشِغَ ثِكِنْ تٜىٰنْتِ عِنْدَ عَكَ أَجِيٜىٰ عَݣُوتِنْ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَ نَ يَهْوٜىٰهْ يَذَوْنَ أَغَبَنْ يَهْوٜىٰهْ يَيِ أَدُّعَ يَثٜىٰ، «وَنٜىٰنٜىٰنِے، يَا يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ ، كُمَ مٜىٰنٜىٰنٜىٰ غِدَانَ حَرْ دَ كَطَغَمُ ذُوَا وَنَّنْ مَڟَيِ؟
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sarki Dawuda kuwa ya shiga alfarwa, ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Wane ne ni, ya Ubangiji Allah, mene kuma gidana da za ka yi mini haka?