1 Chronicles 21:12 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
shekara uku na yunwa, wata uku na shan ɗibga a gaban abokan gābanka, sa’ad da za su bi suna kakkashe ku, ko kuwa kwana uku na takobin Ubangiji, ranakun annoba a cikin ƙasar, mala’ikan Ubangiji zai hallaka kowane sashe na Isra’ila.’ Yanzu sai ka yanke shawara yadda zan amsa wa wanda ya aiko ni.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
كُواْ كَذَاٻِ شٜىٰكَرُ عُكُ نَيُنْوَ، كُواْ وَتَنِّ عُكُ نَمُوغُوَرْ ٻَرْنَ دَغَ أَبُواْكَنْ غَابَنْكَ، سَعَدَّ ذَاسُبِے سُنَ كَكَّشٜىٰكُ، كُواْ كُوَ ݣُونَكِے عُكُ نَمُوغُنْ بَلَعِ عَڧَسَرْ دَغَ حَنُّنْ يَهْوٜىٰهْ ؞ تُواْ، إِنَ سُواْ كَبَانِ أَمْسَرْ دَ ذَنْ كَيْوَ وَنْدَ يَعَيْكٜىٰنِ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
ko shekara uku na yunwa, ko kuwa ka sha ɗibga a hannun maƙiyanka har wata uku, maƙiyanka su yi ta fafararka, ko kwana uku na takobin Ubangiji, wato annoba ke nan da zai aukar wa ƙasar, mala'ikan Ubangiji zai yi ta hallakarwa ko'ina a ƙasar Isra'ila. Yanzu fa, sai ka yi tunani, ka ba ni amsar da zan mayar wa wanda ya aiko ni.”