1 Chronicles 21:16 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Dawuda ya ɗaga ido ya ga mala’ikan Ubangiji tsaye tsakanin sama da duniya, da takobi a zāre a hannunsa ya miƙa a kan Urushalima. Sai Dawuda da dattawa, saye da rigunan makoki suka fāɗi rubda jiki.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَاوُدَ يَطَغَ عِدُوانْسَ يَغَ مَلاَىِٕكَنْ يَهْوٜىٰهْ يَنَ ڟَيٜىٰ أَسَرَرِنْ سَمَ دَ تَكُواْبِے أَ ذَارٜىٰ أَ حَنُّنْسَ، يَنَ مِيڧٜىٰ شِ بِسَ عُرُوشَلِيمَ؞ سَيْ دَاوُدَ دَ دَتَّاوَنْ إِسْرَٰٓءِيلَ سَنْيٜىٰ دَ رِيغُنَنْ نُونَ بَڧِنْ ثِكِ سُكَ ڢَاطِ دَ ڢُسْكُواْكِنْسُ حَرْ ڧَسَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Dawuda ya ɗaga idonsa, sai ya ga mala'ikan Ubangiji yana tsakanin sama da ƙasa, da takobinsa a zare a hannunsa a kan Urushalima. Sa'an nan Dawuda tare da dattawa suka fāɗi rubda ciki, suna saye da tufafin makoki.