1 Chronicles 21:17 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Dawuda ya ce wa Allah, “Ba ni ba ne na umarta a ƙidaya mayaƙan? Ni ne wanda ya yi zunubin da kuma abin da ba daidai ba. Waɗannan dai tumaki ne. Me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, bari hannunka ya fāɗi a kaina da kuma iyalina, amma kada ka bar wannan annoba ya kasance a kan mutanenka.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَنً دَاوُدَ يَثٜىٰ وَ اللَّهْ «أَيْ، نِنٜىٰ نَا بَادَ عُمَرْنِ عَڧِرْغَ مُتَنٜىٰ؞ نِنٜىٰ مَيْ لَيْڢِے، نِنٜىٰ نَا عَيْكَتَ وَنَّنْ مُغُنْتَا؞ عَمَّا وَطَنَّنْ مُتَنٜىٰ كَمَرْ تُمَكِنٜىٰ؞ مٜىٰنٜىٰنٜىٰ سُكَيِ؟ يَا يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نَا، إِنَضُواْڧُواْ، بَرِ حَنُّنْكَ يَڢَاطِ عَكَيْنَ دَ دَنْغِنْ بَابَنَ؞ عَمَّا كَدَ كَبَرْ وَنَّنْ بَلَعِ يَكَسَنْثٜىٰ عَكَنْ مُتَنٜىٰنْكَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Dawuda ya ce wa Allah, “Ai, ni ne na ba da umarni a ƙidaya jama'ar. Hakika, ni na yi zunubi, na kuwa aikata mummunan abu, amma waɗannan talakawa fa, me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, ka bar hannunka ya yi gāba da ni da gidan tsohona, amma kada ka yi gāba da jama'arka, har da za ka aukar musu da annoba.”