1 Chronicles 22:9 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma za ka haifi ɗa wanda zai zama mutumin salama da kuma hutu, zan kuma ba shi hutu daga dukan abokan gābansa a kowane gefe. Za a kira shi Solomon, zai kuma kawo wa Isra’ila salama da natsuwa a zamanin mulkinsa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَهْوٜىٰهْ يَا كُمَ ثٜىٰمِنِ ذَاعَ حَيْڢَ مِنِ طَا؞ طَنَّنْ ذَيْ كَسَنْثٜىٰ مَيْ سَلَمَ؞ غَمَا شِے يَهْوٜىٰهْ ذَيْبَاشِ ذَمَنْ لَاڢِيَ دَ دُكَنْ أَبُواْكَنْ غَابَنْسَ دَسُكٜىٰ كٜىٰوَيٜىٰ دَشِ؞ ذَاعَكِرَا سُونَنْسَ سُلَيْمَٰنُ؞ عَثِكِنْ دُكَنْ ݣُونَكِنْسَ، يَهْوٜىٰهْ يَثٜىٰ، ذَيْسَا ڧَسَرْ إِسْرَٰٓءِيلَ تَكَسَنْثٜىٰ ثِكِنْ سَلَمَ دَ ذَمَنْ لَاڢِيَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Za a haifa maka ɗa, zai zama mutumin salama. Zan kuwa ba shi zaman lafiya da abokan gāba da suke kewaye da shi, gama za a ce da shi Sulemanu, wato salama. Zan kawo wa Isra'ila salama, da natsuwa a zamaninsa.