1 Chronicles 28:8 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Saboda haka yanzu ina umartanku a gaban dukan Isra’ila da na taron jama’ar Ubangiji, da kuma a kunnuwan Allahnmu. Ku yi hankali ku kiyaye dukan umarnan Ubangiji Allahnku don ku mallaki wannan kyakkyawar ƙasa ku kuma bar wa zuriyarku gādo har abada.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«سَبُواْدَ حَكَ، مُتَنٜىٰنَ، أَغَبَنْ تَارُوانْ جَمَعَرْ نَنْ نَدُكَنْ إِسْرَٰٓءِيلَ مُتَنٜىٰنْ يَهْوٜىٰهْ دَ كُمَ أَغَبَنْ اللَّهْ نْمُ، إِنَ كِرَنْكُ كُيِ بِيَيَّ دَ دُكَنْ دُواْكُواْكِنْ دَ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكُ يَعُمَرْثٜىٰكُ؞ تَهَكَ ذَاكُ عِيَ مَلَّكِ ڧَسَرْ نَنْ حَرْ كُإِيَ بَا یَیَنْكُ مُلْكِنْتَ تَغَادُواْ حَرْ أَبَدَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Saboda haka a gaban dukan Isra'ila, wato taron jama'ar Ubangiji, da kuma gaban Allahnmu, sai ku kiyaye, ku bi dukan umarnan Ubangiji Allahnku don ku mallaki ƙasan nan mai kyau, ku kuma bar wa 'ya'yanku ita gādo har abada.