1 Chronicles 29:1 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan Sarki Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ɗana Solomon, wanda Allah ya zaɓa, matashi ne, kuma bai gogu ba. Aikin yana da yawa, domin wannan ƙasaitaccen ginin ba na mutum ba ne, na Ubangiji Allah ne.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَنً سَرْكِے دَاوُدَ يَيِ مَغَنَ غَ دُكَنْ تَارُوانْ جَمَعَ يَثٜىٰ «طَانَ سُلَيْمَٰنُ، شِے وَنْدَ اللَّهْ يَذَاٻَا، سَوْرَيِ نٜىٰ، وَيُوانْ رَايُوَا بَيْ إِشٜىٰشِيبَ تُكُنَ؞ غَاشِ، عَيْكِنْ كُمَ يَنَدَ يَوَ سُواْسَيْ، غَمَا وَنَّنْ هَيْكَلِبَ وُرِنْ دَ مُتُمْ ذَيْ ذَوْنَ بَنٜىٰ، عَمَّا وُرِے نٜىٰ عِنْدَ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ ذَيْ كَسَنْثٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sarki Dawuda fa ya yi magana da dukan taron, ya ce, “Ga shi, ɗana Sulemanu, wanda Allah ya zaɓa, shi dai saurayi ne tukuna, bai gogu da duniya ba tukuna, aikin kuwa babba ne, gama Haikali ba na mutum ba ne, amma na Ubangiji Allah ne.