1 Chronicles 29:20 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ku yabi Ubangiji Allahnku.” Saboda haka suka yabi Ubangiji Allah na kakanninsu; suka rusuna suka kuma fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji da kuma sarki.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَنً دَاوُدَ يَثٜىٰ وَدُكَنْ تَارُوانْ جَمَعَ «كُيَبِے يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكُ؞» سَيْ دُكَنْ جَمَعَ سُكَ يَبِے يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نَكَاكَنِّنْسُ؞ سُكَ رُسُنَ حَرْ ڧَسَا أَغَبَنْ سَرْكِے دَ كُمَ أَغَبَنْ يَهْوٜىٰهْ ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan Dawuda ya ce wa taro duka, “Sai ku yabi Ubangiji Allahnku yanzu.” Taron jama'a kuwa suka yabi Ubangiji Allah na kakanninsu, suka rusuna har ƙasa, suka yi wa Ubangiji sujada, suka kuma girmama sarki.