1 Chronicles 5:26 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Saboda haka Allah na Isra’ila ya zuga ruhun Ful sarkin Assuriya (wato, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya), wanda ya kwashe mutanen Ruben, mutanen Gad da rabin kabilar Manasse zuwa zaman bauta. Ya kwashe su zuwa Hala, Habor, Hara da kuma kogin Gozan, inda suke har wa yau.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَبُواْدَ حَكَ، سَيْ اللَّهْ نَ إِسْرَٰٓءِيلَ يَسَا سَرْكِے ڢُلْ نَ أَسُّرِيَ، وَتُواْ سَرْكِے تِغْلَتْ ڢِلٜىٰسٜىٰرْ نَ أَسُّرِيَ، يَݣُوشِ مُتَنٜىٰنْ ذُرِيَرْ رَعُبَيْنُ دَ نَ غَدْ دَ نَرَبِنْ ذُرِيَرْ مَنَسّٜىٰ نَغَبَسْ ذُوَا بَوْتَا؞ يَكَيْسُ غَرِنْ هَلَ دَ يَنْكِنْ هَبُوارْ دَ هَرَ دَ كُمَ بَاكِنْ كُواْغِنْ غُواْظَنْ، عِنْدَ سُكٜىٰ هَرْوَيَوْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Don haka Allah na Isra'ila ya zuga Ful, Sarkin Assuriya, wato Tiglat-filesar, ya zo ya kwashe su, ya kai su bauta, wato su Ra'ubainawa, da Gadawa, da rabin kabilar Manassa. Ya kai su Hala, da Habor, da Hara, har zuwa kogin Gozan, can suke har yau.