1 Corinthians 1:2 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, da waɗanda aka tsarkake cikin Kiristi Yesu, aka kuma kira domin su zama masu tsarki, tare da dukan waɗanda suke ko’ina da suke kiran sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, Ubangijinsu da kuma namu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ذُوَاغَ جَمَعَرْ مَاسُبِنْ اللَّهْ وَدَّ تَكٜىٰ أَ كُواْرِنْتِ، ذُوَاغَ وَطَنْدَ عَكَ كٜىٰٻٜىٰسُ دَ ڟَرْكِے ثِكِنْ أَلْمَسِيحُ عِيسَىٰ ، ذُوَا كُمَ غَ وَطَنْدَ عَكَ كِرَا سُذَمَ ڟَرْكَكَا ثِكِنْ عِيسَىٰ أَلْمَسِيحُ ، تَرٜىٰدَ دُكَنْ وَطَنْدَ عَكُواْعِنَ سُكٜىٰ أَدُّعَ دَ سُونَنْ عِيسَىٰ أَلْمَسِيحُ عُبَنْغِجِنْمُ ، عُبَنْغِجِنْسُ دَ نَامُ دُكَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Koranti, wato, su waɗanda aka keɓe a cikin Almasihu Yesu, tsarkaka kirayayyu, tare da dukan waɗanda a ko'ina suke addu'a, da sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu, Ubangijinsu da namu duka.