1 Corinthians 12:28 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A cikin ikkilisiya, da farko dai Allah ya zaɓa waɗansu ya naɗa su su zama manzanni, na biyu annabawa, na uku malamai, sa’an nan masu yin ayyukan banmamaki, sai masu baiwar warkarwa, da masu taimakon waɗansu, da masu baiwar gudanarwa, sa’an nan kuma masu magana da harsuna iri-iri.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَثِكِنْ جَمَعَرْ مَاسُبِے، اللَّهْ يَسَا مَنْذَنِّے سُذَمَ نَڢَرْكُواْ، أَنَّبَاوَا سُذَمَ نَبِيُ، مَاسُ كُواْيَرْوَا كُمَ سُذَمَ نَعُكُ، سَيْ مَاسُ يِنْ أَيُّكَنْ بَنْ مَامَاكِ، سَيْ مَاسُ بَيْوَرْ وَرْكٜىٰوَ دَ مَاسُ تَيْمَكُواْ دَ مَاسُ كُلَ دَ عَيْكِنْ جَمَعَرْ مَاسُبِے دَ كُمَ مَاسُ مَغَنَ دَ هَرْسُنَ إِرِ إِرِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A cikin ikkilisiya, Allah ya sa waɗansu su zama, na farko manzanni, na biyu annabawa, na uku masu koyarwa, sa'an nan sai masu yin mu'ujizai, sai masu baiwar warkarwa, da mataimaka, da masu tafiyar da Ikkilisiya, da kuma masu magana da harsuna iri iri.