1 Corinthians 4:9 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Gama a ganina fa, Allah ya baje mu manzanni a ƙarshen jerin gwanon, a matsayin mutanen da aka hukunta ga mutuwa a filin wasanni. Mun zama abin kallo ga dukan duniya, ga mala’iku da kuma mutane.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
غَمَا أَغَنِينَ، اللَّهْ يَنُونَ أَڢِيلِ ثٜىٰوَ مُو مَنْذَنِّے مُو نٜىٰ نَڧَرْشٜىٰ عَكُواْمٜىٰ، كَمَرْ وَطَنْدَ عَكَ يَنْكٜىٰوَ حُكُنْثِنْ مُتُوَ، دُوانْ مُو مُنْذَمَ أَبِنْدَ دُونِيَا دُكَ دَ مَلاَىِٕكُ دَ مُتَنٜىٰ ذَاسُ سَاوَ عِدُواْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Don a ganina, Allah ya bayyana mu, mu manzanni, koma bayan duka ne, kamar waɗanda mutuwa yake jewa a kansu, don mun zama abin nuni ga duniya, da mala'iku duk da mutane.