1 John 5:20 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Mun san cewa Ɗan Allah ya zo duniya, ya kuma ba mu ganewa domin mu san shi wanda yake na gaskiya. Mu kuwa muna cikinsa, shi da yake Allah na gaskiya wato, cikin Ɗansa Yesu Kiristi. Shi ne Allah na gaskiya da kuma rai na har abada.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مُنْ سَنِ ثٜىٰوَ طَنْ اللَّهْ يَا ذُواْ دُونِيَا، يَا كُمَ بَامُ غَانٜىٰوَ دُواْمِنْ مُسَنْ شِے وَنْدَ يَكٜىٰ نَغَسْكِيَ؞ مُو كُوَ مُنَ ثِكِنْسَ، شِے دَيَكٜىٰ نَغَسْكِيَ وَتُواْ، ثِكِنْ طَنْسَ عِيسَىٰ أَلْمَسِيحُ ؞ شِينٜىٰ اللَّهْ نَغَسْكِيَ دَ كُمَ رَيْ نَهَرْ أَبَدَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Mun kuma sani Ɗan Allah ya zo, ya yi mana baiwar fahimta domin mu san shi wanda yake na gaskiya. Mu kuwa muna a cikinsa, shi da yake na gaskiya, wato Ɗansa Yesu Almasihu. Shi ne Allah na gasikya da kuma rai madawwami.