1 Kings 12:16 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Da dukan Isra’ila suka ga sarki ya ƙi yă saurare su, sai suka amsa wa sarki, “Ina ruwanmu da Dawuda! Ai! Ba mu da gādo wurin ɗan Yesse. Ya Isra’ila, kowa yă koma tentinsa! Dawuda, sai ka lura da gidanka!” Saboda haka Isra’ilawa suka watse zuwa gida.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا سَعَدَّ إِسْرَٰٓءِيلَ دُكَ سُكَغَ ثٜىٰوَ سَرْكِے بَيْ سَوْرَرٜىٰسُبَ، سَيْ مُتَنٜىٰنْ سُكَ أَمْسَوَ سَرْكِے سُكَثٜىٰ، «إِنَا ضُوَنْمُ دَ دَاوُدَ! أَيْ! بَامُ دَ غَادُواْ أَوُرِنْ طَنْ يٜىٰسّٜىٰ؞ يَا إِسْرَٰٓءِيلَ، كُواْوَ يَكُواْمَ تٜىٰنْتِنْسَ! يَا دَاوُدَ، سَيْكَلُورَ دَ غِدَنْكَ؞» دُواْمِنْ حَكَ مُتَنٜىٰنْ إِسْرَٰٓءِيلَ سُكَ وَڟٜىٰ، كُواْوَ يَكُواْمَ غِدَنْسَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Da mutanen Isra'ila suka ga sarki ya ƙi jin roƙonsu, sai suka yi ihu, suna cewa, “A yi ƙasa da Dawuda da iyalinsa. Me suka taɓa yi mana? Mazajen Isra'ila, bari duka mu tafi gida! Mu bar Rehobowam ya lura da kansa!” Jama'ar Isra'ila fa suka tayar,