1 Kings 12:21 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Da Rehobowam ya isa Urushalima, ya tattara dukan gidan Yahuda da kabilar Benyamin, ya sami sun kai mayaƙa dubu da tamanin. Sai aka shirya don su yaƙi gidan Isra’ila, su kuma mayar da masarautar wa Rehobowam ɗan Solomon.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ رٜىٰهُواْبُواْوَمْ يَ إِسُواْ عُرُوشَلِيمَ، سَيْ يَتَارَ سُواْجُواْجِ مَڢِيَ عِيَ يَاڧِ دُبُو طَرِے دَ دُبُو تَمَٰنِنْ دَغَ غِدَنْ يَهُودَ دَ نَ بِلِيَامِنُ؞ عَكَ شِرْيَ كَيْ وَ غِدَنْ إِسْرَٰٓءِيلَ يَاڧِ، دُواْمِنْ أَ مَيْدَسُو ڧَرْڧَشِنْ مُلْكٍ رٜىٰهُواْبُواْوَمْ طَنْ سُلَيْمَٰنُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Da Rehobowam ya komo Urushalima, sai ya tara dukan jama'ar gidan Yahuza, da na kabilar Biliyaminu. Aka sami mayaƙa dubu ɗari da dubu tamanin (180,000) waɗanda za su yi yaƙi da gidan Isra'ila, don su komar da su a ƙarƙashin mulkin Rehobowam, ɗan Sulemanu.