1 Kings 13:2 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai mutumin Allah ya tā da murya a kan bagade bisa ga umarnin Ubangiji ya ce, “Ya bagade, bagade! Ubangiji ya ce, ‘Za a haifi ɗa mai suna Yosiya wa gidan Dawuda. A kanka zai miƙa firistoci na masujadai kan tuddai masu miƙa hadayu a nan, za a kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kanka.’ ”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يَطَغَ مُرْيَ يَيِ أَنَّبْثِنْ غَابَادَ بَغَدٜىٰ بِسَغَ مَغَنَرْ يَهْوٜىٰهْ يَثٜىٰ «كَيْ بَغَدٜىٰ، كَيْ بَغَدٜىٰ، إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ ، ‹ذَاعَ حَيْڢِ طَا أَ ذُرِيَرْ دَاوُدَ، مَيْ سُونَ يُواْسِيَا؞ ذَيْ مِيڧَ هَدَايَ عَكَنْكَ؞ سُو ڢِرِسْتُواْثِے نَوَطَنْسُ وُرَارٜىٰنْ سُجَّدَ، وَطَنْدَ سُكَ ڧُواْنَ تُرَارٜىٰ عَكَنْكَ، سُونٜىٰ ذَاعَ مِيڧَسُ هَدَايَ؞ ذَاعَكُمَ ڧُواْنٜىٰ ڧَسُسُوَنْ یَنْ أَدَمْ عَكَنْكَ؞› »
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Bisa ga umarnin Ubangiji, sai annabin ya ta da murya, ya ce, “Ya bagade, bagade, Ubangiji ya ce za a haifi ɗa a gidan Dawuda, sunansa Yosiya wanda zai miƙa firistoci na masujadan tuddai hadaya a kanka, wato firistoci waɗanda suke ƙona turare. Za a ƙone ƙasusuwan mutane a bisa kanka.”