1 Kings 13:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Ka roƙi Ubangiji Allahnka, ka kuma yi addu’a domina don hannuna ya warke.” Saboda haka mutumin Allah ya yi roƙo ga Ubangiji, hannun sarki kuwa ya warke, ya kuma zama kamar yadda yake a dā.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ سَرْكِے يٜىٰرُواْبُواْوَمْ يَثٜىٰ وَمُتُمِنْ اللَّهْ نَّنْ «كَضُواْڧَا مِنِ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكَ، كَيِ مِنِ أَدُّعَ دُواْمِنْ هَنُّونَ يَدَاوُاْ دَيْدَيْ؞» مُتُمِنْ اللَّهْ كُوَ يَضُواْڧِ يَهْوٜىٰهْ ، سَيْ حَنُّنْ سَرْكِے يَوَرْكٜىٰ، يَكُواْمَ كَمَرْ يَدَّ دَا يَكٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sarki Yerobowam ya ce wa annabin, “In ka yarda ka yi roƙo ga Ubangiji Allahnka domina, ka yi mini addu'a don ya warkar da hannuna.” Annabi ya roƙi Ubangiji, sai hannun sarki ya komo daidai.