1 Kings 14:15 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ubangiji kuma zai bugi Isra’ila, har tă zama kamar kyauro mai girgiza a bakin rafi. Zai tumɓuke Isra’ila daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba wa kakanninsu, yă watsar da su gaba da Kogin Yuferites domin sun tsokane Ubangiji har ya yi fushi, ta wurin yin ginshiƙan Ashera.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
نِے يَهْوٜىٰهْ ذَنْ بُغِ إِسْرَٰٓءِيلَ، ذَاتَيِ ضَوَ كَمَرْ ثِيَوَ عَبَاكِنْ ضُوً رَاڢِ؞ ذَنْ تُمْٻُكٜىٰ مُتَنٜىٰنْ إِسْرَٰٓءِيلَ دَغَ ڧَسَا مَيْݣَوْ طِنَّنْ دَ نَبَا كَاكَنِّنْسُ، ذَنْ كُمَ وَرْوَاڟَرْ دَسُو عَيَنْكِنْ ڧٜىٰتَرٜىٰنْ كُواْغِنْ يُڢِرٜىٰتِسْ، سَبُواْدَ سُنْ سَا نَيِ ڢُشِے تَوُرِنْ يِنْ غُنْكِنَّنْ مَيْ سُونَ أَشٜىٰرَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji zai hukunta Isra'ila kamar yadda akan girgiza iwa a baƙin rafi, zai tumɓuke Isra'ila daga wannan ƙasa mai albarka wadda ya ba kakanninsu, ya kuma watsar da su a hayin Kogin Yufiretis, domin sun yi wa kansu gumaka don sun tsokani Ubangiji ya yi fushi.