1 Kings 15:22 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ سَرْكِے أَسَ يَيِ شٜىٰلَ كُواْعِنَ أَ يَهُودَ ثٜىٰوَ كُواْوَ يَڢِتُواْ، كُمَ بَابُوَنْدَ عَكَ وَارٜىٰ، كُواْوَ يَتَيْمَكَ عَكْوَاشِ دُوَڟُو دَ كَتَكَنْ دَ بَعَشَ يَيِ أَمْڢَانِ دَسُو دُواْمِنْ ڠَرَنْ رَمَ؞ أَسَ يَيِ أَمْڢَانِ دَ كَايَنَّنْ يَڠَغْڠَرَ بِرْنِنْ غٜىٰبَ عَيَنْكِنْ بِلِيَامِنُ دَ كُمَ مِظْڢَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan sarki Asa ya gayyaci dukan jama'ar Yahuza, ba wanda aka ɗauke wa. Suka tafi suka kwashe duwatsu da katakai waɗanda Ba'asha yake ginin Rama da su. Da su sarki Asa ya gina Geba ta Biliyaminu, da Mizfa.