1 Kings 16:34 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A lokaci Ahab ne, Hiyel mutumin Betel ya sāke gina Yeriko. Ya kafa tushensa a bakin ran ɗan farinsa Abiram, ya kuma kafa ƙofofinsa a bakin ran autansa Segub, bisa ga maganar Ubangiji da ya yi ta wurin Yoshuwa ɗan Nun.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَ زَامَانِنْ مُلْكِنْسَ نٜىٰ هِيٜىٰلْ دَغَ بٜىٰتٜىٰلْ يَغِنَ يٜىٰرِكُواْ؞ دَ يَكَڢَ تُوشٜىٰنْ غِنِنْ، سَيْ طَنْسَ نَڢَارِ، وَتُواْ أَبِرَمْ يَمُتُ؞ دَ يَغَمَ غِنِنْ يَنَ سَا ڧُواْڢُواْڢِنْسَ، سَيْ أَوْتَ ثِكِنْ یَیَنْسَ مَظَا، وَتُواْ سٜىٰغُبْ يَمُتُ؞ وَنَّنْ يَڢَرُ نٜىٰ دُواْمِنْ عَثِكَ مَغَنَرْ يَهْوٜىٰهْ تَبَاكِنْ يُواْشُوَ طَنْ نُنْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A cikin kwanakinsa, Hiyel mutumin Betel ya gina Yariko. Ya yi hasarar ɗan farinsa, Abiram, sa'ad da ya kafa harsashin ginin, ya kuma yi hasarar autansa, Segub, sa'ad da ya sa ƙofofin, kamar yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin Joshuwa ɗan Nun.