1 Kings 17:1 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
To, Iliya mutumin Tishbe, daga Tishbe a Gileyad, ya ce wa Ahab, “Muddin Ubangiji, Allah na Isra’ila wanda nake bauta wa yana a raye, ba za a yi raɓa ko ruwan sama a ’yan shekaru masu zuwa ba, sai ko na faɗa haka.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَنَانً سَيْ وَنِ أَنَّبِے مَيْ سُونَ إِلْيَاسُ دَغَ تِشْبٜىٰ عَيَنْكِنْ غِلٜىٰيَدْ، يَثٜىٰ وَ سَرْكِے أَهَبْ «نَا ضَنْڟٜىٰ دَ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ مَيْ رَيْ نَ إِسْرَٰٓءِيلَ، وَنْدَ نَكٜىٰ بَوْتَا مَسَ، بَذَاعَيِ رَٻَبَ، بَلّٜىٰ ضُوً سَمَ، عَثِكِنْ یَنْ شٜىٰكَرُ مَاسُ ذُوَا، سَيْ كُواْ نَيِ مَغَنَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Wani annabi mai suna Iliya, mutumin Tishbi a Gileyad, ya ce wa sarki Ahab, “Na rantse da Ubangiji, Allah na Isra'ila, wanda nake bauta wa, ba za a yi raɓa ko ruwan sama cikin shekarun nan ba, sai da faɗata.”