1 Kings 17:12 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai ta ce masa, “Na rantse da Ubangiji Allahnka, ba ni da wani abinci, sai dai ɗan gari hannu guda a tulu, da kuma ɗan mai a kwalaba. Ina tattara ’yan itacen nan ne don in kai gida in yi abinci wa kaina da ɗana, don mu ci, mu mutu.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ تَأَمْسَ تَثٜىٰ «نَا ضَنْڟٜىٰ دَ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكَ مَيْ رَيْ، بَانِ دَكُواْمٜىٰ سَيْدَيْ طَنْ غَارِنْ عَبِنْثِ عَتُكُنْيَ دَ طَنْ مَيْ عَتُلُ؞ يَنْذُ إِنَ نٜىٰمَنْ إِتَاثٜىٰنْ دَڢُوَ دَ ذَنْ كَيْ غِدَا إِنْيِ عَبِنْثِ دَشِ، نِے دَ يَرُواْنَ مُثِ مُمُتُ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ta ce, “Na rantse da Ubangiji Allahnka, ba ni da abinci, sai dai ɗan farin da ya ragu a tukunya, da ɗan man da yake cikin kurtu. Ga shi, ina tattara itacen don in je in shirya shi domin ni da ɗana, mu ci. Shi ke nan, ba sauran wani abu kuma, sai mutuwa.”