1 Kings 18:12 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ban san inda Ruhun Ubangiji zai kai ka sa’ad da na bar ka ba. In na tafi na faɗa wa Ahab bai kuma same ka a nan ba, zai sa a kashe ni. Tuna fa, ni bawanka, na yi wa Ubangiji sujada tun ina saurayi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
غَاشِ دَظَرَرْ نَبَرْكَ رُوحٌ يَهْوٜىٰهْ ذَيْ طَوْكٜىٰكَ ذُوَا وَنِ وُرِنْ دَ بَنْ سَنِبَ؞ أَيْ، عِدَنْ نَا ڢَطَا وَ أَهَبْ كَنَ أَنَنْ، بَيْ كُمَذُواْ يَسَامٜىٰكَبَ، ذَيْسَا عَكَشٜىٰنِ؞ تُنَ ڢَا، نِے مَيْ ڟُواْرُوانْ يَهْوٜىٰهْ نٜىٰ تُنْ إِنَ يَرُواْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Rabuwata da kai ke da wuya, sai Ruhun Ubangiji ya kai ka wurin da ban sani ba, don haka, in na tafi na faɗa wa Ahab, in bai same ka ba, to, ni zai kashe, ko da yake ni baranka, tun ina saurayi nake tsoron Ubangiji.