1 Kings 18:21 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Iliya ya je gaban mutane ya ce, “Har yaushe za ku yi ta yawo tsakanin ra’ayoyi biyu? In Ubangiji ne Allah, ku bi shi; amma in Ba’al Allah ne, ku bi shi.” Mutane dai ba su ce uffam ba.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ إِلْيَاسُ يَمَڟُواْ كُسَدَ دُكَنْ مُتَنٜىٰنْ يَثٜىٰمُسُ «دُوانْمٜىٰ كُكٜىٰ رَبَ حَنْكَلِنْكُ بِيُ؟ عِدَنْ يَهْوٜىٰهْ شِينٜىٰ اللَّهْ ، كُبِے شِ؞ عَمَّا عِدَنْ بَعَلْ شِينٜىٰ اللَّهْ ، سَيْ كُبِے شِ؞ عَمَّا مُتَنٜىٰنْ بَسُ ثٜىٰ مَسَ كُواْمٜىٰبَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Iliya kuwa ya zo kusa da jama'a ya ce, “Har yaushe za ku daina yawo da hankalinku? Idan Ubangiji shi ne Allah, to, ku bauta masa, in kuwa Ba'al ne Allah, to, ku bauta masa.” Mutane duk suka yi tsit, ba su ce uffan ba.