1 Kings 18:36 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A lokacin hadaya, sai annabi Iliya ya zo gaba ya yi addu’a, ya ce, “Ya Ubangiji Allah na Ibrahim, na Isra’ila da kuma na Yaƙub, bari a sani a yau cewa kai Allah ne a cikin Isra’ila, a kuma san cewa ni bawanka ne, na kuma yi dukan waɗannan abubuwa bisa umarninka.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ لُواْكَثِنْ يِنْ هَدَايَ تَيَمَّ يَيِ، سَيْ أَنَّبِے إِلْيَاسُ يَمَڟُواْ كُسَ يَثٜىٰ «يَا يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نَ إِبْرَٰهِيمْ دَ نَ إِسْحَٰڧَ دَ نَ يَعْڧُوبَ، كَسَا أَ سَنِ يَوْ ثٜىٰوَ كَيْنٜىٰ اللَّهْ نَ إِسْرَٰٓءِيلَ، نِنٜىٰ كُمَ بَاوَنْكَ، نَاكُوَيِ وَنَّنْ دُكَ بِسَغَ مَغَنَرْكَ نٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A lokacin miƙa hadaya ta maraice, sai annabi Iliya ya matso kuwa, ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Ibrahim, da Ishaku, da Isra'ila, bari ya zama sananne a wannan rana, cewa kai ne Allah a Isra'ila, ni kuma bawanka ne, na yi waɗannan abubuwa duka bisa ga maganarka.