1 Kings 19:10 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya amsa, ya ce, “Ina kishi dominka Ubangiji, Allah Maɗaukaki. Isra’ilawa sun ƙi alkawarinka, suka rurrushe bagadanka, suka kuma kashe annabawanka da takobi. Ni ne kaɗai na rage, yanzu, ni ma suna ƙoƙari su kashe ni.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِلْيَاسُ يَثٜىٰ «دَڨُوذُواْ سُواْسَيْ نَبَوْتَا مَكَ، يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ مَيْ ضُنْدُنَا؞ عَمَّا مُتَنٜىٰنْ إِسْرَٰٓءِيلَ سُنْ كَرْيَ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَرْكَ، سُكَ رُشٜىٰ بَغَدٜىٰنْكَ، سُكَ كَكَّشٜىٰ أَنَّبَاوَنْكَ دَ تَكُواْبِے؞ نِنٜىٰ كَطَيْ نَضَغٜىٰ؞ يَنْذُ سُنَ نٜىٰمَ سُكَشٜىٰنِ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya amsa ya ce, “Ya Ubangiji, Allah Mai Runduna, kai kaɗai nake bauta wa kullayaumin. Amma jama'ar Isra'ila sun karya alkawarinka, sun rurrushe bagadanka, sun karkashe annabawanka, ni ne kaɗai na ragu, ga shi kuma, suna nema su kashe ni.”