1 Kings 19:21 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Elisha ya bar shi, ya koma, ya ɗauki shanunsa ya yayyanka. Ya ƙone kayan garman noman don yă dafa naman, ya kuma ba wa mutane naman, suka kuwa ci. Sa’an nan ya tashi, ya bi Iliya, ya kuma zama mai hidimarsa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَلْيَسَعَ يَكُواْمَ يَطَوْكِ شَانُنْ دَيَكٜىٰ نُواْمَ دَسُو يَيَنْكَ، يَيِ أَمْڢَانِ دَ غُنْ‌غُمٜىٰنْ وُيَنْ شَانُنْ نُواْمَ يَدَڢَ نَامَنْ، يَبَا مُتَنٜىٰ، سُكَثِ؞ سَيْ يَكُواْمَ يَبِے إِلْيَاسُ يَنَيِ مَسَ حِدِمَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Elisha kuwa ya koma, ya kama shanun noman, ya yanka, ya dafa su da karkiyoyinsu. Ya raba wa mutane, suka ci. Sa'an nan ya tashi, ya bi Iliya, ya zama mai taimakonsa.