1 Kings 19:4 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Shi kuma ya yi tafiya yini guda zuwa cikin hamada. Ya zo wurin wani itacen tsintsiya, ya zauna a ƙarƙashinsa, ya roƙa yă mutu. Ya ce, “Ya ishe ni haka, Ubangiji, ka ɗauki raina; ban fi kakannina ba.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا إِلْيَاسُ يَوُثٜىٰ؞ دَ يَيِ تَڢِيَ تَرَانَ غُدَا ثِكِنْ دَاجِ، يَكَيْ وُرِنْ وَنِ إِتَاثٜىٰ يَذَوْنَ أَغِنْدِنْسَ؞ سَيْ إِلْيَاسُ يَيِ أَدُّعَ يَثٜىٰ «يَا يَهْوٜىٰهْ ، كُواْمٜىٰ يَ إِشٜىٰنِ؞ بَرِ كَطَوْكِ رَيْنَ، غَمَا بَنْڢِے كَاكَنِّنَ وَطَنْدَ سُكَ مُتُبَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Iliya ya yi tafiyarsa yini guda cikin jeji, ya tafi ya zauna a gindin wani itace ya yi roƙo domin ya mutu, yana cewa, “Yanzu ya isa haka, ya Ubangiji, ka karɓi raina, gama ban fi kakannina ba.”