1 Kings 2:19 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ بَتْشٜىٰبَةُ تَتَڢِے وُرِنْ سَرْكِے سُلَيْمَٰنُ دُواْمِنْ تَيِ مَغَنَ دَشِ أَمَدَدِنْ أَدُواْنِيَ؞ سَرْكِے كُوَ يَتَاشِ دَغَ كَنْ كُجٜىٰرَرْ مُلْكِنْسَ دُواْمِنْ يَمَرَبْثٜىٰتَ، يَرُسُنَ أَغَبَنْتَ؞ دَ يَذَوْنَ، سَيْ يَسَا عَكَ كَٰوُاْ مَتَ وَتَ كُجٜىٰرَرْ مُلْكِ، تَا كُوَ ذَوْنَ تَهَنُّنْ دَامَنْسَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan Bat-sheba ta tafi wurin sarki Sulemanu don ta yi magana da shi a kan Adonija. Sarki ya tashi domin ya tarye ta. Ya rusuna mata, sa'an nan ya zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo mata kujera, ta kuwa zauna a wajen damansa.