1 Kings 2:26 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا سَرْكِے يَثٜىٰ وَ أَبِيَتَرْ ڢِرِسْتِ «كَكُواْمَ غِدَنْكَ عَثَنْ غَرِنْ أَنَتُواتْ؞ كَا ثَنْثَنْثِ مُتُوَ، عَمَّا بَذَنْ كَشٜىٰكَ يَنْذُ بَ، سَبُواْدَ كَكَنْ طَوْكِ عَݣُوتِنْ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَ نَ عُبَنْ‌غِجِ يَهْوٜىٰهْ أَغَبَنْ بَابَنَ دَاوُدَ، كُمَ دُكَنْ وَهَلُواْلِنْ دَ سُكَ ڢُسْكَنْثِ بَابَنَ، كَجِمْرٜىٰ تَرٜىٰدَشِ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sarki kuma ya ce wa Abiyata, firist, “Ka koma ƙasarka ta gādo a Anatot, gama ka cancanci mutuwa, amma yanzu ba zan kashe ka ba domin ka ɗauki akwatin alkawari na Ubangiji Allah a gaban Dawuda, tsohona, domin kuma ka sha wahala duka tare da tsohona.”