1 Kings 2:4 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَنً يَهْوٜىٰهْ ذَيْثِكَ أَلْڧَوَرِنْسَ دَ يَيِ مِنِ ثٜىٰوَ ‹عِدَنْ یَیَنْكَ سُنَ لُورَ دَ حَنْيَرْسُ، سُنَ تَڢِيَ دَ أَمِنْثِ أَغَبَنَ دَ دُكَنْ ذُوثِيَارْسُ دَ كُمَ دُكَنْ رَنْسُ، بَذَاعَ رَسَ مُتُمْ دَغَ ثِكِنْ یَیَنْكَ وَنْدَ ذَيْ ذَوْنَ عَكُجٜىٰرَرْ مُلْكِنْكَ عَ إِسْرَٰٓءِيلَ بَ؞›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
domin Ubangiji ya cika maganar da ya faɗa mini cewa, ‘Idan 'ya'yanka suna lura da hanyarsu, sun yi tafiya a gabana da gaskiya da zuciya ɗaya, da dukan ransu, ba za ka rasa mutum wanda zai hau gadon sarautar Isra'ila ba.’