1 Kings 20:28 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai mutumin Allah ya zo ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Domin Arameyawa suna tsammani Ubangiji allahn tuddai ne, ba allahn kwari ba, zan ba da wannan ɗumbun mayaƙa a hannuwanka, za ka kuwa sani ni ne Ubangiji.’ ”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ مُتُمِنْ اللَّهْ يَذُواْ وُرِنْ سَرْكِنْ إِسْرَٰٓءِيلَ يَثٜىٰ «إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ ، ‹سَبُواْدَ سُرِيَاوَا سُنْثٜىٰ نِے يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نَكَنْ تُدَّيْ نٜىٰ، بَنَوُرِنْ دَيَكٜىٰ ڢِيلِ، تُواْ، ذَنْبَادَ يَوَنْ جَمَعَرْ نَنْ أَ حَنُّنْكَ، ذَاكَ كُوَ سَنِ ثٜىٰوَ نِنٜىٰ يَهْوٜىٰهْ ؞› »
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Annabin Allah kuwa ya je wurin Sarkin Isra'ila ya ce masa, “Ubangiji ya ce, ‘Tun da yake Suriyawa sun ce, Ubangiji shi Allah na tuddai ne, ba Allah na kwari ba, saboda haka zan ba da dukan wannan taron jama'a a hannunka, za ka sani ni ne Ubangiji.’ ”