1 Kings 20:34 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ben-Hadad ya ce, “Zan mayar da biranen mahaifinka da na ƙwace daga mahaifinka. Za ka iya sa wurin kasuwarka a cikin Damaskus, kamar yadda mahaifinka ya yi a Samariya.” Ahab ya ce, “Bisa wannan yarjejjeniya zan sake ka.” Saboda haka ya yi yarjejjeniya da shi, sai ya bar shi ya tafi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَنً بٜىٰنْهَدَدْ يَثٜىٰ وَ أَهَبْ «ذَنْ كُواْمَرْ مَكَ دَ غَرُضُوً دَ بَابَنَ يَڨُوثٜىٰ دَغَ حَنُّنْ بَابَنْكَ؞ كَنَ كُمَ عِيَ كَڢَ وَكَنْكَ وُرَارٜىٰنْ كَاسُوَنْثِ أَ دِمَشْڧُ، كَمَرْ يَدَّ بَابَنَ يَيِ أَ سَمَرِيَ؞» سَيْ أَهَبْ يَثٜىٰ مَسَ «ذَنْ بَرْكَ كَتَڢِے بِسَغَ يَدَّ مُكَ يَرْدَ؞» سُكَيِ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَ سَيْ عَكَ سَكِ بٜىٰنْهَدَدْ يَتَڢِے؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ben-hadad ya ce masa, “Biranen da tsohona ya ƙwace daga wurin tsohonka, zan mayar maka. Kai kuma za ka yi karauku a Dimashƙu kamar yadda tsohonka ya yi a Samariya.” Sai Ahab ya ce, “Zan bar ka, ka tafi a kan wannan sharaɗi.” Ya kuwa yi alkawari da shi, sa'an nan ya bar shi, ya tafi.