1 Kings 21:15 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Nan da nan sa’ad da Yezebel ta ji cewa an jajjefe Nabot da dutse ya kuma mutu, sai ta ce wa Ahab, “Tashi ka mallaki gonar inabin Nabot mutumin Yezireyel wanda ya ƙi ya sayar maka. Ba shi da rai, ya mutu.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَظَرَرْ يٜىٰظٜىٰبٜىٰلْ تَكَرْٻِ سَڧُوانْ ثٜىٰوَ أَنْرِغَا أَنْجٜىٰجّٜىٰڢِ نَبُواتْ حَرْ يَمُتُ، تَثٜىٰ وَ أَهَبْ «تَاشِ! تَڢِے كَمَلَّكِ غُواْنَرْ دَ نَبُواتْ مُتُمِنْ يٜىٰظِرٜىٰيٜىٰلْ يَڧِ يَسَيَرْ مَكَ، غَمَا نَبُواتْ بَاشِ دَ رَيْ، يَمُتُ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Nan da nan da Yezebel ta ji an jajjefi Nabot har ya mutu, sai ta ce wa Ahab, “Tashi, ka mallaki gonar inabin Nabot, wadda ya ƙi sayar maka, gama Nabot ba shi da rai, ya mutu.”