1 Kings 22:8 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sarkin Isra’ila ya amsa wa Yehoshafat, ya ce, “Akwai mutum guda har yanzu wanda ta wurinsa za mu iya nemi nufin Ubangiji, amma na ƙi jininsa domin bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni ba, sai dai mummuna kullum. Shi ne Mikahiya ɗan Imla.” Yehoshafat ya ce, “Kada sarki ya ce haka.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَرْكِے أَهَبْ نَ إِسْرَٰٓءِيلَ يَأَمْسَ مَسَ يَثٜىٰ «عِ، أَݣَويْ وَنِنْ دَ ذَامُ عِيَ نٜىٰمَنْ نُڢِنْ يَهْوٜىٰهْ تَوُرِنْسَ، سُونَنْسَ مِكَيَ طَنْ إِمْلَ؞ عَمَّا بَانَ سُوانْسَ، سَبُواْدَ بَايَ أَنَّبْثِ مَيْݣَوْ عَكَيْنَ، سَيْدَيْ مَسِيڢَ؞» سَرْكِے يٜىٰهُواْشَڢَتْ نَ يَهُودَ يَثٜىٰ «سَرْكِے، كَدَ كَيِ مَغَنَ حَكَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sarkin Isra'ila ya ce wa Yehoshafat, “Da sauran mutum ɗaya wanda za mu iya mu tambaya faɗar Ubangiji, shi ne Mikaiya ɗan Imla, amma ina ƙinsa, gama bai taɓa yin wani annabcin alheri a kaina ba, sai dai na masifa.” Yehoshafat ya ce, “Kada sarki ya faɗi haka.”