1 Kings 4:21 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Solomon kuwa ya yi mulki a bisa dukan masarautai daga Kogi zuwa ƙasar Filistiyawa, har zuwa iyakar Masar. Waɗannan ƙasashe sun yi ta kawo haraji, suka kuma zama bayin Solomon dukan kwanakin ransa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَرْكِے سُلَيْمَٰنُ يَيِ مُلْكِ عَبِسَ دُكَنْ مُلْكُواْكِنْ أَلْعُمَّيْ دَغَ كُواْغِنْ يُڢِرٜىٰتِسْ أَغَبَسْ ذُوَا ڧَسَرْ ڢِلِسْتِيَ عَيَمَّ حَرْ إِيَاكَرْ ڧَسَرْ مَصَرْ؞ سُكَيِ تَبِيَ مَسَ هَرَاجِنْسُ، سُكَ بَوْتَا مَسَ دُكَنْ ݣُونَكِنْ رَنْسَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sulemanu ya sarauci dukan mulkoki tun daga Kogin Yufiretis a gabas, har zuwa ƙasar Filistiyawa a yamma, daga kudu kuma har zuwa iyakar Masar. Su kuwa suka yi ta kawo wa Sulemanu harajinsu, ya kuwa mallake su dukan kwanakin ransa.