1 Kings 5:9 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ma’aikatana za su gangara da su daga Lebanon zuwa bakin teku. Zan sa a ɗaɗɗaura su su bi ruwan teku daga Lebanon zuwa bakin Bahar Rum da za ka nuna mini. A can zan kunce maka su, sa’an nan ka kwashe. Kai kuma za ka biya bukatata ta wurin tanadin abinci wa gidana.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مَعَيْكَتَنَ ذَاسُ غَنْ‌غَرُواْ دَسُو ذُوَا بَاكِنْ تٜىٰكُ؞ ذَنْسَا أَطَطَّوْرٜىٰسُ سُبِے ضُوً تٜىٰكُ دَغَ لٜىٰبَنُوانْ ذُوَا بَاكِنْ تٜىٰكُنْ دَ ذَاكَ نُونَ مِنِ؞ أَوُرِنْ ذَنْ كُنْثٜىٰ مَكَسُ، سَعَنً كَݣُوشٜىٰ؞ كَيْ كُمَ ذَاكَ بِيَ بُڧَاتَتَ تَوُرِنْ تَنَدِنْ عَبِنْثِنْ غِدَانَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Barorina za su kawo su daga Lebanon zuwa teku. Zan sa a yi gadon fito da su, su bi teku zuwa inda kake so, a can mutanena za su warware su, sa'an nan naka mutane su kwashe su. Kai kuma ka ba da abinci ga mutanena.”