1 Kings 8:66 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A rana ta biye sai ya sallame mutane. Suka sa wa sarki albarka, sa’an nan suka watse zuwa gida, da farin ciki, da murna a zukatansu saboda kyawawan abubuwan da Ubangiji ya yi domin bawansa Dawuda, da kuma mutanensa Isra’ila.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَ رَانَ تَتَݣُوسْ، سَيْ سُلَيْمَٰنُ يَسَلَّمِ مُتَنٜىٰنْ سُكَ تَڢِے؞ مُتَنٜىٰ دُكَ سُكَ يَبِے سَرْكِے، سُكَ كُواْمَ غِدَاجٜىٰنْسُ دَ ڢَضٍ ثِكِ دَ مُرْنَ سَبُواْدَ أَبُبُوَ مَاسُ ݣَوْ دَ يَهْوٜىٰهْ يَيِ وَبَاوَنْسَ دَاوُدَ دَ كُمَ جَمَعَرْسَ إِسْرَٰٓءِيلَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A rana ta takwas ya sallami jama'ar, su kuwa suka yabi sarki. Sa'an nan suka kama hanyar gidajensu suna murna, suna farin ciki saboda dukan alherin da Ubangiji ya yi wa bawansa, Dawuda, da jama'arsa, Isra'ilawa.