1 Kings 9:16 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
(Fir’auna sarkin Masar ya kai wa Gezer hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Ya sa mata wuta, ya kashe Kan’aniyawanta mazaunan wurin, ya kuma ba da ita a matsayin kyautar aure ga ’yarsa, matar Solomon.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَا سَرْكِنْ مَصَرْ يَڢَاطَوَ غٜىٰظٜىٰرْ يَثِسُ دَ يَاڧِ، يَكَكَّشٜىٰ كَنْعَنِيَاوَنْ دَسُكٜىٰ ثِكِنْ بِرْنِنْ، يَكُمَ ڧُواْنٜىٰ بِرْنِنْ؞ سَعَنً يَبَا یَرْسَ بِرْنِنْ يَذَمَ مَتَ ݣَوْتَرْ عَوْرٜىٰ سَعَدَّ تَ عَوْرِ سُلَيْمَٰنُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Gama Fir'auna ya haura, ya ci Gezer, ya ƙone ta da wuta, ya kuma kashe masu zama cikinta. Sa'an nan ya yi wa 'yarsa, wato matar Sulemanu, kyauta da Gezer ɗin.