1 Peter 2:5 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
ku ma, a matsayinku na duwatsu masu rai, ana gina ku ga zama gidan ruhaniya don ku zama tsattsarkar ƙungiyar firistoci, kuna miƙa hadayun ruhaniya, abin karɓa ga Allah ta wurin Yesu Kiristi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
كُو كُوَ كَمَرْ دُوَڟُو مَاسُ رَيْ نٜىٰ وَطَنْدَ عَكٜىٰ أَمْڢَانِ دَسُو دُواْمِنْ أَغِنَ غِدَا إِرِنَّرُوحُ دَ نُڢِ ثٜىٰوَ كُيِ حِدِمَ كَمَرْ ڧُنْ‌غِيَرْ ڢِرِسْتُواْثِے مَاسُ ڟَرْكِے عَثِكِنْ وَنَّنْ غِدَا، كُنَ مِيڧَ مَسَ هَدَايُ نَرُوحُ إِرِنْ وَنْدَ اللَّهْ يَكٜىٰ كَرْٻَ، تَوُرِنْ عِيسَىٰ أَلْمَسِيحُ ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ku kuma, kamar rayayyun duwatsu, bari a gina gida mai ruhu da ku, domin ku zama tsattsarkar ƙungiyar firistoci, da nufin ku miƙa hadayu na ruhu, abin karɓa ga Allah, ta wurin Yesu Almasihu,