1 Peter 2:9 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma ku zaɓaɓɓu ne, ƙungiyar firistocin babban Sarki, al’umma mai tsarki, jama’a mallakar Allah, domin ku shaida yabon shi wanda ya kira ku daga cikin duhu zuwa haskensa mai banmamaki.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا كُو ڧَبِيلَثٜىٰ وَدَّ اللَّهْ يَذَاٻَا، كُمَ ڧُنْغِيَرْ ڢِرِسْتُواْثِثٜىٰ تَ اللَّهْ بَبَّنْ سَرْكِے، أَلْعُمَّثٜىٰ مَيْ ڟَرْكِے، كُمَ جَمَعَرْ اللَّهْ تَمُسَمَّنْ دُواْمِنْ كُيِ شٜىٰلَرْ مَنْيَنْ أَلْعَمُرَنْسَ نَبَنْ مَامَاكِ نَوَنْدَ يَكِرَاكُ دَغَ ثِكِنْ دُهُ، كُكَ شِغَ ثِكِنْ حَصْكٜىٰنْسَ نَبَنْ مَامَاكِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Amma ku kabila ce zaɓaɓɓiya, ƙungiyar firistocin babban Sarki, tsattsarkar al'umma, jama'ar mallakar Allah, domin ku sanar da mafifitan al'amuran wannan da ya kirawo ku daga cikin duhu, kuka shiga maɗaukakin haskensa.