1 Samuel 1:11 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ta yi ta cewa, “Ya Ubangiji Maɗaukaki. In har ka dubi baƙin cikin baiwarka, ka tuna da ni, ba ka kuma manta da baiwarka ba, amma ka ba ta ɗa, ni ma zan miƙa shi ga Ubangiji dukan rayuwarsa, aska kuwa ba za tă taɓa kansa ba.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
هَنَّةُ تَيِ ضَنْڟُوَا تَثٜىٰ «يَا يَهْوٜىٰهْ مَيْ إِيكُواْ دُكَ ، عِدَنْ كَدُوبِے وَهَلَرْ بَيْوَرْكَ حَرْ كَتُنَ دَنِے، بَكَمَنْتَادَنِے بَ، كَبَانِ طَا، تُواْ، سَيْ إِنْبَادَشِ غَ يَهْوٜىٰهْ دُكَنْ ݣُونَكِنْ رَايُوَرْسَ، كُمَ بَذَاعَ أَسْكٜىٰ كَنْسَبَ كُواْ كَطَنْ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ta yi wa'adi, ta ce, “Ya Ubangiji Mai Runduna, idan lalle ka dube ni, ni baiwarka, ka tuna da ni, ba ka manta da ni baiwarka ba, amma ka ba ni ɗa, ni ma sai in ba da shi ga Ubangiji dukan kwanakinsa, aska kuwa ba za ta taɓa kansa ba.”