1 Samuel 1:19 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Kashegari da sassafe suka tashi suka yi sujada a gaban Ubangiji, sai suka koma garinsu a Rama. Elkana kuwa ya kwana da matarsa Hannatu, Ubangiji kuma ya tuna da ita.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
وَشٜىٰغَرِ سَيْ دُكَنْ عِيَلِنْ سُكَتَاشِ دَ سَسَّڢٜىٰ سُكَيِ وَ يَهْوٜىٰهْ سُجَّدَ؞ سَعَنً سُكَ كُواْمَ غِدَنْسُ أَ رَمَ؞ دَ عٜىٰلْكَنَ يَݣُونَ دَ مَاتَرْسَ هَنَّةُ، سَيْ يَهْوٜىٰهْ يَأَمْسَ أَدُّعَرْتَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Elkana da iyalinsa suka tashi tun da sassafe suka yi wa Ubangiji sujada, sa'an nan suka koma gidansu a Rama. Elkana fa ya kwana da matarsa, Hannatu. Ubangiji kuwa ya tuna da ita.