1 Samuel 14:47 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Bayan Shawulu ya hau karagar mulkin Isra’ila, ya yi yaƙi da abokan gābansu ta kowane gefe. Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, sarakunan Zoba, da kuma Filistiyawa. Duk wurin da ya juya, ya hore su.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ طَالُوتَ يَذَمَ سَرْكِنْ إِسْرَٰٓءِيلَ، يَيِ يَاڧِ دَ أَبُواْكَنْ غَابَنْ إِسْرَٰٓءِيلَ وَطَنْدَ سُكٜىٰ كٜىٰوَيٜىٰ دَشِ؞ يَيِ يَاڧِ دَ مُواْوَبْ دَ أَمُّوانْ دَ عٜىٰدُوامْ دَ سَرَاكُنَنْ ذُوابَ دَ ڢِلِسْتِيَاوَا؞ دُكْ عِنْدَ طَالُوتَ يَتَڢِے يَاڧِ، يَيِ نَصَرَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'ad da Saul ya ci sarautar Isra'ila, ya yi yaƙi da dukan abokan gābansa da suke kewaye da shi. Ya yi yaƙi da Mowabawa da Ammonawa, da Edomawa, da sarakunan Zoba, da Filistiyawa. Duk inda ya yi yaƙi ya sami nasara.