1 Samuel 16:2 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma Sama’ila ya ce, “Yaya zan yi haka? Ai, in Shawulu ya ji labari, zai kashe ni.” Ubangiji ya ce, “To, sai ka tafi tare da ’yar karsana ka ce, ‘Na zo don in yi wa Ubangiji hadaya.’
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا سَمَٰعِيلَ يَثٜىٰ «يَيَ ذَنْيِ حَكَ؟ عِدَنْ طَالُوتَ يَجِ ذَيْ كَشٜىٰنِ؞» يَهْوٜىٰهْ يَأَمْسَ يَثٜىٰ «تُواْ، كَطَوْكِ یَرْ سَانِيَ تَرٜىٰدَكَيْ، عِدَنْ كَا إِسُواْ سَيْ كَثٜىٰ كَاذُواْ مِيڧَ هَدَايَ غَ يَهْوٜىٰهْ ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sama'ila kuwa ya ce, “Ƙaƙa zan yi wannan? Gama idan Saul ya ji zai kashe ni.” Sai Ubangiji ya ce, “Ka tafi da ɗan maraƙi, ka ce, ka zo ne ka miƙa wa Ubangiji hadaya.