1 Samuel 16:4 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sama’ila kuwa ya yi abin da Ubangiji ya umarce shi. Da ya isa Betlehem, sai dattawan garin suka tarye shi da rawar jiki, suka ce masa, “Mai duba, wannan ziyara lafiya dai ko?”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَمَٰعِيلَ يَيِ أَبِنْدَ يَهْوٜىٰهْ يَعُمَرْثٜىٰشِ؞ دَ يَشِغَ بَيْتَلَحْمِ، سَيْ دَتَّاوَنْ غَرِنْ سُكَ مَرَبْثٜىٰشِ دَ ضَوَرْ جِكِے؞ سُكَ تَمْبَيٜىٰشِ سُكَثٜىٰ «لَاڢِيَ دَيْ كَذُواْ؟»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sama'ila ya yi yadda Ubangiji ya faɗa masa, ya tafi Baitalami, inda dattawan garin suka tarye shi da rawar jiki, suka ce masa, “Maigani, wannan ziyara lafiya kuwa?”