1 Samuel 16:5 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sama’ila ya ce, “I, lafiya ƙalau. Na zo ne domin in yi wa Ubangiji hadaya. Ku tsarkake kanku sa’an nan ku zo mu tafi wurin yin hadaya tare.” Ya kuma sa Yesse da ’ya’yansa maza su tsarkake kansu, su je wurin hadayar.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَأَمْسَ يَثٜىٰ «عِ، لَاڢِيَ لَوْ؞ نَا ذُواْ يِنْ هَدَايَ نٜىٰ غَ يَهْوٜىٰهْ ؞ كُكٜىٰٻٜىٰ كَنْكُ دَ ڟَرْكِے، كُذُواْ تَرٜىٰدَنِ وُرِنْ هَدَايَ؞» سَمَٰعِيلَ كُوَ يَڟَبْتَثٜىٰ يٜىٰسّٜىٰ دَ یَیَنْسَ مَظَا؞ سَعَنً يَغَيَّثٜىٰسُ ذُوَا وُرِنْ هَدَايَرْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya ce, “I, lafiya lau. Na zo ne in miƙa wa Ubangiji hadaya, sai ku tsarkake kanku, ku zo mu tafi wurin yin hadaya tare.” Ya kuma sa Yesse da 'ya'yansa maza su tsarkake kansu, su je wurin hadayar.