1 Samuel 17:49 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya sa hannu a jakarsa ya ɗauki dutse, ya sa cikin majajjawa ya wurga, dutsen kuwa ya bugi Bafilistin a goshi, dutsen ya shiga cikin goshinsa, sai Bafilistin ya fāɗi rubda ciki.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يَسَا حَنُّ أَ جَكَرْسَ يَڢِتَرْدَ دُوڟٜىٰ، يَسَا أَ مَجَجَّوَرْسَ يَجٜىٰڢِ جَالُوتَ دَشِ؞ دُوڟٜىٰنْ يَهَرْبِے جَالُوتَ مُتُمِنْ ڢِلِسْتِيَ أَغُواْشِنْسَ حَرْ يَشِغَ ثِكِنْ غُواْشِنْسَ؞ مُتُمِنْ كُوَ يَڢَاطِ دَ ڢُسْكَرْسَ حَرْ ڧَسَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan Dawuda ya ɗauko dutse daga cikin angararsa, ya wurga, dutsen kuwa ya sami Goliyat a goshi, har ya lume. Goliyat kuwa ya faɗi rubda ciki.