1 Samuel 19:5 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya yi kasai da ransa sa’ad da ya kashe Bafilistin nan. Ubangiji ya ba wa dukan Isra’ila babban nasara, ka gani, ka kuma yi farin ciki. Don me za ka ci mutuncin amintaccen mutum kamar Dawuda ta wurin kashe shi ba tare da wani dalili ba?”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَسَدَوْكَرْ دَ رَنْسَ لُواْكَثِنْدَ يَكَشٜىٰ جَالُوتَ؞ رَانَرْ نَنْ يَهْوٜىٰهْ يَا كَٰوُاْ بَبَّنْ ثٜىٰتُواْ غَ دُكَنْ إِسْرَٰٓءِيلَ؞ كَيْ مَا دَ كَغَ وَنَّنْ كَيِ مُرْنَ؞ تُواْ، دُوانْمٜىٰ يَنْذُ كَكٜىٰسُواْ كَيِ وَمَيْ أَمِنْثِ لَيْڢِے؟ كَدَ كَكَشٜىٰ دَاوُدَ بَابُ دَلِيلِ!»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya yi kasai da ransa har ya kashe Bafilisten, Ubangiji kuwa ya ba Isra'ilawa babbar nasara. Kai ma ka gani, ka kuwa yi murna. Me ya sa za ka ɗauki alhakin Dawuda, wanda bai yi maka laifin kome ba?”