1 Samuel 2:1 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Hannatu ta yi addu’a ta ce, “Zuciyata tana farin ciki a cikin Ubangiji; a cikin Ubangiji an sa ina jin daɗi ƙwarai. Na buɗe bakina na yi wa abokan gābana dariya. Kai! Ina murna domin ka cece ni!
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ هَنَّةُ تَيِ أَدُّعَ تَثٜىٰ، «ذُوثِيَاتَ تَثِكَ دَ ڢَضٍ ثِكِ سَبُواْدَ يَهْوٜىٰهْ ؞ يَهْوٜىٰهْ يَاسَا إِنَجِ دَڧَرْڢِے سُواْسَيْ؞ نَبُوطٜىٰ بَاكِنَ نَيِ وَ أَبُواْكَنْ غَابَنَ دَارِيَا؞ كَيْ! إِنَمُرْنَ دُواْمِنْ كَثٜىٰثٜىٰنِ!
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Hannatu kuwa ta yi addu'a ta ce, “Ubangiji ya cika zuciyata da murna. Ina farin ciki da abin da ya yi. Ina yi wa maƙiyana dariya, Ina matuƙar murna domin Allah ya taimake ni.